Riyad Maharez zai raba gari da Leicester City
Dan wasan tsakiya na kungiyar Leicester City, Riyad Maharez, ya amince da sauya sheka zuwa kungiyar kwallon kafa ta Arsenal a kan kudi fan miliyan 35.
Wallafawa ranar:
A watannin baya, rahotanni sun tabbatar da cewa kungiyar Barcelona, ta yi kokarin saye shi daga Leicester, amma daga bisani maganar ta lafa.
Tayin farko da kungiyar Arsenal ta yiwa Maharez, shi ne na rattaba hannu kan yarjejeniyar buga mata wasanni, tsawon shekaru hudu, wanda kuma ya amince da hakan.
A makon da ya gabata, an rawaito cewa dan wasan gaba na Arsenal Alexis Sanchez, ka iya sauya sheka zuwa kungiyar Manchester City, wanda hakan yasa wasu masharhanta ke ganin zai iya haifar wa da Arsenal nakasu wajen zura kwallaye.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu