Isa ga babban shafi
Wasanni-Najeriya

Tawagar Najeriya ta kwallon kafar rairayi ta tafi Bahamas

Tawagar Najeriya ta kwallon kafar Yashi ko bakin teku, ta tashi zuwa birnin Bahamas na Amurka, inda zata fafata a gasar cin kofin kwallon kafar yashin ta duniya da za’a fara daga ranar 27 ga watan Afrilu zuwa 7 ga watan Mayu.

Tawagar kwallon kafar yashi ta Najeriya.
Tawagar kwallon kafar yashi ta Najeriya. sportloaded.com
Talla

Kakakin hukumar kula da kwallon kafar Najeriya NFF Ademola Olajire ya ce ‘yan wasa 8 daga cikin 12 ne suka samu tafiyar karkashin mai horarwa Audu Adamu, yayinda sauran hudun zasu baya a ranar talata mai zuwa saboda jinkirin da aka samu wajen karba musu takardar Visa.

Yayin gasar kwallon yashin da ta gudana a shekara 2011 a kasar Italiya, Najeriya ta kammala gasar ce a matsayi na 7.

Najeriya na rukuni na biyu tare da Mexico, Italiya da kuma Iran.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.