Tawagar Najeriya ta kwallon kafar rairayi ta tafi Bahamas
Tawagar Najeriya ta kwallon kafar Yashi ko bakin teku, ta tashi zuwa birnin Bahamas na Amurka, inda zata fafata a gasar cin kofin kwallon kafar yashin ta duniya da za’a fara daga ranar 27 ga watan Afrilu zuwa 7 ga watan Mayu.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kakakin hukumar kula da kwallon kafar Najeriya NFF Ademola Olajire ya ce ‘yan wasa 8 daga cikin 12 ne suka samu tafiyar karkashin mai horarwa Audu Adamu, yayinda sauran hudun zasu baya a ranar talata mai zuwa saboda jinkirin da aka samu wajen karba musu takardar Visa.
Yayin gasar kwallon yashin da ta gudana a shekara 2011 a kasar Italiya, Najeriya ta kammala gasar ce a matsayi na 7.
Najeriya na rukuni na biyu tare da Mexico, Italiya da kuma Iran.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu