Isa ga babban shafi
Wasanni-India

India ta jajirce wajen kwarewa a wasan kwallon kafa

Mai horar da tawagar kwallon kafar kasar India, Stephen Constantine ya bayyana kwakkwaran yakini kan samun nasarar kasar wajen halartar gasar cin kofin nahiyar Asiya da za’a yi a shekara ta 2019. 

Tawagar 'yan wasan kwallon kafa ta kasar India.
Tawagar 'yan wasan kwallon kafa ta kasar India. deccanchronicle.com
Talla

Kasar India, wadda ta samu halartar gasar har sau 3, tana cikin rukunin farko a wasannin neman cancantar zuwa gasar tare da kasashen Myanmar, Macau da kuma Kyrgyztan, inda ake bukatar kasashe biyu su samu zuwa gasar.

A wasan farko da ya gudana, India ta samu nasarar kan Myammar da 1-0 a satin da ya gabata.

A wani cigaban kuma ana sa ran wasan sada zumuncin da India ta lallasa kasar Cambodia da 3-2, ya taimaka mata matsawa gaba daga matakin kasa ta 132 wajen iya kwallon kafa a duniya zuwa gaba.

A watan da ya gabata ne hukumar FIFA ta bayyan cewa zata maida hankali wajen bunkasa wasan kwallon kafa a kasar India, wadda ‘yan kasar suka fi maida hankali kan wasan Cricket.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.