Isa ga babban shafi
Wasanni

Senegal ce ke jan ragamar jadawalin FIFA a Afirka

Hukumar Fifa ta fitar da jadawalin kasashen da suka fi iya taka leda a duniya, kamar yadda ta sa ba lokaci zuwa lokaci,a Nahiyar Afrika Senegeal ce ke kan gaba a wannan lokaci, inda ta doke Ivory Coast da ke rike da kambun Nahiyar Afrika.

Tawagar 'yan wasan Sénégal
Tawagar 'yan wasan Sénégal AFP PHOTO/MONIRUL BHUIYAN
Talla

Jawadalin da ta fitar na wannan Disambar, ya ce Senegal ce ta farko kuma ta 33 a Duniya, yayin da Ivory coast ke bi mata a mataki na Biyu kuma na 34 a duniya.

Tunisia ce ta Uku a Afrika sai Masara ta 4, Algeria ta 5, DR Congo ta 6, Burkina Faso ta 7, Najeriya ce ta 8 kuma ta 51 a duniya, sai Ghana da ke na 9 a Afrika ta 53 a Duniya, Moroko ke matakin na 10 a jadawalin.

Dukkanin wadanan kasashe dai na cikin kasashe 16 da zasu fafata da junan a gasar cin kofin nahiyar Afrika da Gabon za ta dauki nauyi tsakanin 14 ga watan Janairu zuwa 5 ga watan Fabiru mai zuwa a birnin Libreville.

A duniya gaba daya kuwa Argentina ta ci gaba da zama ta daya a jerin gwanayen tamaular.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.