An biya Super Falcons na Najeriya kudinsu
‘Yan wasan Super Falcons na Najeriya sun fice daga Otel din Agura da a baya suka ce, ba za su fice ba har sai gwamnati ta biya su kudadensu na alawus bayan sun lashe kofin gasar kwallon Afrika ta mata a Kamaru.
Wallafawa ranar:
Shugaba Muhammadu Buhari ne ya bayar da umarnin a biya ‘yan wasan bayan sun gudanar da zanga-zanga a kofar majalisar tarraya ta kasar da nufin janyo hankalin shugaban da ke halartar majalisar a ranar.
Ministan wasanni da matasa na kasar Barr.Solomon Dalung, ya bayyana wa sashin hausa na RFI cewa, an bai wa kowacce daga cikin matan Naira miliyan 8.
A farko dai, 'yan matann sun jajirce cewa dole ne gwamnati ta biya kowacce daga cikin su kimanin Naira miliyan 11, kudaden da suka hada da bashin da suke bi a can baya da kuma na yanzu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu