An fara gyara wa Super Eagles filin wasa na Uyo
Hukumomin Najeriya sun fara aikin gyare-gyare a filin wasa na Gods Will Akpabio da ke Uyo gabanin karawar da tawagar kasar za ta yi da Algeria a gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya.
Wallafawa ranar:
Dama dai hukumar kwallon kafar kasar ta bayar da tabbacin cewa, za ta bukaci gwamnatin jihar Akwa Ibom da ta gyara filin wasan sakamakon korafin da ‘yan wasan Super Eagles suka yi, in da suka koka kan rashin kyawun filin wasan.
‘Yan wasan dai ba su ji dadin yadda suka kara da Tanzania ba a cikin watan jiya a wannan filin a gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar Afrika saboda rashin kyawun sa.
A ranar 12 ga watan gobe ne dai, Najeriya za ta fafata da Algeria a filin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu