Joe Hart zai koma Torino
A yau talata za a gwada lafiyar Mai tsaron raga Manchester City, Joe Hart, a kulob din Torino na Seria A, da City ke shirin baiwa aronsa.
Wallafawa ranar:
Kungiyar kwallon kafar ta bashi daman barin Ingila tun jiya litinni zuwa Italiya.
Hart, mai shekaru 29, Kocin City Pep Guardiola ya bashi daman tafiya duk inda yake so.
Zuwa 31 ga watan Agusta da za a rufe kasuwar cinikin ‘yan wasanni, ake saran a kamala kula kwantiragi da dan wasan da zai tsarewa Ingila raga a ranar lahadi
A makon daya gabata, Kocin Everton Ronald Koeman, yayi watsi da rade-rade da akeyi cewa Hart zai koma kungiyarsa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu