Isa ga babban shafi
Wasanni

Portugal ta tsallaka gaba a gasar Euro 2016

Dan wasan Portugal Christiano Ronaldo ya kara samun kwarin gwiwa dangane da fafutukarsa ta neman lashe wa kasarsa kofin gasar kasashen Turai da ake yi a Faransa.

Cristiano Ronaldo na Portugal na neman lashe wa kasarsa gasar cin kofin kasashen Turai a bana
Cristiano Ronaldo na Portugal na neman lashe wa kasarsa gasar cin kofin kasashen Turai a bana REUTERS/Darren Staples
Talla

Wannan kuma na faruwa ne bayan Portugal ta samu nasara akan Poland a bugun fanafreti 5-3 a wasan da suka buga a jiya a Marseille, lamarin da ya bai wa Portugal damar tsallaka wa matakin wasan dab da na karshe a gasar ta Euro 2016, yayin da Poland ta fice daga gasar.

Kafin aje ga bugun fanariti sai da kasashen biyu suka buga 1-1 kuma Poland ce ta fara zura kwallo ta hannun Robert Lewandowski a mintina na biyu da fara wasan amma daga bisani Portugal ta farke ta hannun Renato Sanches.

Yanzu haka dai Portugal za ta hadu da Wales ko kuma Belgium.

In anjima ne kasashen Wales da Belgium din za su fafata da juna a matakin wasan dab da na karshe, yayin da kocin tawagar Wales, Chris Coleman ya bayyana cewa, karawarsu ta yau, ita ce mafi muhimmanci a gare su tun lokacin gasar cin kofin duniya wadda aka gudanar a shekara ta 1958.

Kasar dai ba ta taba samun gurbi a matakin wasan karshe na wata babbar gasa ba, tun lokacin da Brazil ta doke ta shekaru 58 da suka gabata a gasar cin kofin duniya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.