Isa ga babban shafi
wasanni

PSG zata taimaka wa 'yan gudun hijiran da suke tsallaka zuwa Turai

Kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint-Germain ko PSG, dake rike da kambin gasar Lig din Faransa tace zata bayar da gudunmawar kudi EURO miliyon 1, ga wasu kugiyoyi, ta hannun gidauniyar kungiyarta da aka kaddamar don taimaka wa ‘yan gudun hijiran dake kwarara zuwa kasashen Turai.

'Yan wasan kungiyar PSG, lokacin da suka lashe kofi
'Yan wasan kungiyar PSG, lokacin da suka lashe kofi REUTERS/Charles Platiau
Talla

Kungiyar zata yi haka ne don ganin ‘yan gudun hijirar sun sami sabuwar rayuwa a nahiyar Turai.
Wannan matakin da kungiyar ta dauka na zuwa ne bayan wasu manyan kungiyoyin na kwallon kafa a sassan duniya daban daban, kamr su Real Madrid ta Spain, Roma Italiya da Bayern Munich kasar Jamus, sun bayyana aniyar taimakawa ‘yan gudun hijiran, da akasarinsu suka fito daga kasar Syria, da yaki ya daidaita.
Yanzu haka dai kasashen na turai suna ci gaba da samar da hoyoyin karbar ‘yan gudun hijiran.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.