Froome ya lashe Tour de France
Dan tseren keken Birtaniya Chris Froome shi ne ya lashe gasar tseren keke ta Tour de France da aka kammala a jiya Lahadi, kuma wannan ne karo na biyu da ya lashe doruwar riga bayan ya lashe gasar a 2013.
Wallafawa ranar:
Dan wasan na kungiyar Sky dai ya sha zargi kan shan kwayu ma su kuzari
A mataki na 14 dan wasan ya ce wasu ‘Yan kallo sun watsa masa fitsari akan zargin da suke ma sa yana shan kwaya don samun kuzari,
An dade dai ana zargin ‘yan tseren keke da Matsalar kwankwadar kwayu, Sai dai wasu na ganin an samu tsabta a gasar sabanin shekarun baya inda har aka karbe wa Lance Armstrong nasarorinsa guda 7 da ya samu a gasar Tour de France.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu