Isa ga babban shafi
Wasanni

UEFA na tattauna hanyar rage kudadden da Kulob din Turai ke kashe wa

Hukumar kwallon kafar Nahiyar Turai UEFA, ta fara wani zaman tattaunawa domin samar da haske a kan yadda Kulob din Turai ke kashe kudadensu.Tsarin da hukumar ke fatan gani an samu sauyi a kai karkashin jagoranci shugabanta Micheal Platini zai taimakawa kungiyoyi da dama.

Shugaban hukumar 'UEFA, Michel Platini
Shugaban hukumar 'UEFA, Michel Platini REUTERS/Ruben Sprich
Talla

Idan aka cimma matsaya Kungiyoyin irinsu Manchester city da Paris saint Germain PSG wanda suka fi kowani kungiya kwallon kafa, kashe kudi a turai za su rage adaddin kudadden da suke karkashe wa.

Platini dai ya jima yana alkawarin samar da sauyi a harkan kwallon kafar turai, wanda shine baban batu  da yake fatan ya samar da sauyi a kai.

Yanzu dai haka akwai Kungiyoyin kwallayen kafa 14 a turai da ake son tsarin ya fara aiki a kan su.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.