2013: Gasar Cin kofin Afrika
Wannan ne karo na 29 da za’a gudanar da gasar Cin kofin Afrika a 2013 a kasar Afrika ta Kudu wanda Hukumar CAF ke daukar nauyin gudanarwa. Duk kasar da ta lashe kofin gasar ita ce zata wakilici Afrika a gasar cin kofin Kalubale tsakanin zakarun kasashen Nahiyoyin Duniya da za’a gudanar a kasar Brazil a 2013.