Jam'iyyun siyasa na tattaunawa don kafa Gwamnati bayan zabe
Jam’iyyar Sinn Fein a kasar Ireland ta zama jam’iyya ta biyu mafi girma a Majalisar dokokin kasar, abinda zai bata damar shiga sabuwar gwamnati a dama da ita.Bayan kamala kidaya kuri’u jiya talata, Sinn Fein ta samu kujeru 37 daga cikin 160 dake Majalisar wakilai, a zaben da mutane sama da kasha 62 suka kada kuri’a.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Jam’iyyar Fianna Fail ke kan gaba da kujeru 38, yayin da Jam’iyyar Firaminista Leo Varadkar ta Fine Gael ke da kujeru 35 a Majalisar.
Tuni aka fara tattaunawa domin kafa sabuwar gwamnati.
Zaben ya kasance zakaran gwajin dafi ga Firaministan kasar tun bayan ficewar Birtaniya daga cikin gungun kasashen Turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu