Isa ga babban shafi
Faransa

Gwamnatin Faransa na kokarin magance rikicin ma'aikatan kasar

Manyan jami’an gwamnatin Faransa sun yi ganawar gaggawa a jiya lahadi don kasance a cikin shirin ko-ta-kwana, yayin da kasar ke shirin fadawa yajin aikin gama gari a ranar alhamis mai zuwa domin nuna rashin amincewa da sabuwar dokar yin ritaya.

Edouard Philippe Firaministan Faransa
Edouard Philippe Firaministan Faransa Philippe LOPEZ / AFP
Talla

Ana hasashen cewa yajin aikin zai yi matukar shafar lamurran yau da kullum a sassan kasar ta Faransa, yayin da shugaban Emmanuel Macron ke ci gaba da kare matakin aiwatar da sauye-sauye ga tsarin zuwa ritaye a kasar.

Firaministan kasar Edouard Philippe da kan sa ne ya jagoranci zaman taron Ministocin na jiya lahadi a Paris.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.