Isa ga babban shafi
London

Maharin London tsohon dan ta'adda ne- 'Yan sanda

Rundunar ‘yan sandan birnin London ta tabbatar da cewa maharin da ya hallaka mutane 2 da wuka cikin daren jiya Juma’a tsohon dan ta’adda ne da aka saki daga gidan yari bara.

Yankin da aka kaddamar da farmakin na wuka a birnin London
Yankin da aka kaddamar da farmakin na wuka a birnin London Reuters/Peter Nicholls
Talla

Maharin wanda aka yi zargin ya na sanye da rigar bom tuni jami’an ‘yan sanda suka harbe shi har lahira yayinda aka garzaya da mutane 3 da suka jikkata a harin asibiti.

‘yansanda dai sun bayyana maharin dan shekaru 28 da suna Usman Khan kuma ya aikata laifuka a kasar da suka kai shi gaz aman yari wanda kuma ya kaddamar da farmakin shekara guda bayan fitowarsa.

Neil Basu, shugaban sashen yaki da ayyukan ta’addanci a Birtaniya, ya ce tuni aka bindige maharin lokacin da ake yunkurin murkushe shi, kuma farmakin nasa ko shakka babu na ta’addanci ne.

Wasu hotuna da aka yada a kafafen sada zumunta, sun nuna wani mutum kwance a kasa amma da wuka rike a hannunsa, yayin da ‘yan sanda dauke da bindigogi ke tsaye a kansa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.