Isa ga babban shafi
Wasanni

Barca na ci gaba da tattaunawa da PSG

Magabatan kungiyoyin Barca da na Paris Saint Germain na ci gaba da tattaunawa bayan wata yar gajeriyar ganawa a jiya talata tsakanin su dangane da batun sayar da dan wasan Brazil Neymar zuwa tsohuwar kungiyar sa ta Barca.

Neymar na Brazil da ke taka leda a PSG ta Faransa
Neymar na Brazil da ke taka leda a PSG ta Faransa REUTERS/Benoit Tessier
Talla

An dai safe makwonni ana tattaunawa tsakanin bangarorin wanda ake kuma ganin cewa ganawar ta jiya talata na tabbatar da ficewar dan wasan zuwa Barcelonna.

A cewar wata jarida mai suna le Parisien, wannan jarida ta tsegunta cewa kungiyar Barca ta shirya domin sayen dan wasan a kan kudi Milyan 170 na Euros.

Kudin da zata biya sau biyu a cewar jaridar tareda bayar da wani dan wasa bayan haka.

A jiya talata an hango Oscar Grau tareda rakiyar Eric Abidal da wasu mukaraban kungiyar ta Barca da suka shiga tattaunawa da Leonardo mai kula da bangaren motsa jiki a kungiyar ta Paris Saint Germain.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.