Isa ga babban shafi
Turai

An fara zaben EU bisa tsoron rinjayen masu tsattsauran ra'ayi

Jam'iyyun da ke kyamar baki a nahiyar Turai na kokarin bayar da mamaki a zaben 'yan Majalisun Tarayyar Turai da za’a fara yau a nahiyar baki daya.

Tambarin zaben kungiyar Tarayyar Turai na 2019
Tambarin zaben kungiyar Tarayyar Turai na 2019 European Union
Talla

Yanzu haka dai a faro zaben ne daga kasashen Birtaniya da Netherlands, kafin sauran kasashen su yi amfani da sauran kwanakin don kada tasu kuri'ar.

Fiye da mutane miliyan 400 ake saran su kada kuri'a a zaben na Majalisar Tarayyar Turai inda za su zabi Yan Majalisu 751 a kasashen nahiyar 28.

Shugabannin kasashen Nahiyar dai Galibi Emmanuel Macron na Faransa da Angela Merkel ta Jamus sun ja hankalin magoya bayansu don kaucewa kin fitowa kada kuri'a a zaben mai matukar muhimmanci, wanda suka ce rashin fitowar jama'a ne ka iya jefa mulkin hannun masu tsattsauran ra'ayi.

A bangare guda Kasar Birtaniya da ke kokarin ficewa daga kungiyar ta EU, Majalisar Turai ta tilasta mata shiga zaben ne bayan rashin amincewar Majalisar kasar  da yarjejeniyar da Theresa May ta kulla da EU kan ficewar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.