Isa ga babban shafi
Faransa

Kan masu zanga-zangar Faransa ya rabu a mako na 13 da fara gangami

Karo na 13 a jere dubban masu zanga-zanga sanye da yaluwar riga a sassan kasar Faransa sun sake fitowa yau Asabar, sai dai a wannan makon adadinsu ya zarta na makon jiya, matakin da ake alakanta da gaza lalubo bakin zaren warware rikicin siyasar kasar.

Dandazon masu zanga-zangar Faransa a yau Asabar 9 ga watan Fabarairu
Dandazon masu zanga-zangar Faransa a yau Asabar 9 ga watan Fabarairu REUTERS/Gonzalo Fuentes
Talla

A makon jiya dai adadin masu zanga-zangar da suka fita titunan kasar ta faransa bai gaza mutum dubu 58 da 600 ba, ko da dai masu zanga-zngar sun yi ikrarin cewa yawansu ya kai dubu 116.

Wani bangare na masu zanga-zangar dai sun nuna bukatar hadewa da kungiyoyin kwadagon kasar don neman biyan bukatarsu da saukaka matsin rayuwa, yayinda jagororin suka tsaya kan bakansu na ganin shugaba Emmanuel Macron ya yi murabus.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.