Taliban za ta halarci tattaunawar sulhu da Afghanistan a Moscow
Rasha ta ce shugaban Afganistan Ashraf Ghani, ya amince zai aika da tawagar manyan jami’an diflomasiyyar kasar domin halartar tattaunawar sulhu da kungiyar Taliban a karkashin jagorancin kasar ta Rasha a birnin Moscow.
Wallafawa ranar:
Wannan dai shi ne karo na farko da sashin diflomasiyyar mayakan Taliban zai halarci irin wannan tattaunawa ta sulhu.
Tun a watan Agustan da ya wuce, Rasha ta yi yunkurin ganin tattaunawar ta gudana, inda ta gayyaci kasashe 12 da kungiyar ta Taliban, amma shugaba Ashraf Ghani yayi watsi da tayin, inda ya ce tilas sai dai tattaunawar ta gudana a karkashin jagorancin Afghanistan.
Ma’aikatar harkokin wajen Rasha ta ce tattaunawar za ta gudana a ranar 9 ga watan Nuwamban da muke ciki.
Wasu daga cikin kasashen da za su tura wakilcinsu wajen tattaunawar sun hada da India, Iran Pakistan, China da kuma Amurka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu