Isa ga babban shafi
Faransa

Macron ya yi wa Ministocinsa garanbawul

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi garambawul a Majalisar Ministocinsa, in da ya nada shugaban Jam’iyyarsa mai mulki, Christophe Castaner a matsayin sabon Ministan Cikin Gida.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron
Shugaban Faransa Emmanuel Macron REUTERS/Pascal Rossignol
Talla

Ana kallon garambawul din a matsayin wani yunkurin Macron na karfafa gwamnatinsa bayan wasu tsoffin ministocinsa da suka hada da na Cikin Gida, Gerard Collomb da na Muhalli, Nicolas Hulot sun yi murabus.

Ministan Kudi, Bruno Le Maire da Ministan Harkokin Waje, Jean Yves Le Drien za su ci gaba da rike mukamansu, yayin da a gefe guda aka nada sabbin Ministocin Noma da na Raya Al’adu.

Kimanin mako guda kenan da ake dakon matakin Macron na garambawul a Majalisar Ministocin nasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.