Faransa ta bukaci a ci gaba da mutunta yarjejeniyar nukiliyar Iran
Shugaban Faransa Emmanuel Macron a ganawar sa da Firaminitan Isra'ila yayi gargadi domin ganin an kaucewa samun tashin hankali sakamakon shirin Iran na cigaba da tace sinadarin uranium domin bunkasa makamashin ta.
Wallafawa ranar:
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu wanda ke ziyarar neman goyan bayan kasashen Turai wajen ganin sun yi watsi da yarjejeniyar Iran, bai samu biyan bukata ba daga shugaban Faransa Emmanuel Macron kamar yada shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta shaida masa.
Firaminista Netanyahu ya cigaba da zargin Iran a matsayin mai nema jefa gabas ta tsakiya da kuma Turai cikin tashin hankali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu