Isa ga babban shafi
Faransa

Ana zargin tsohon minista da karbo kudin yakin neman zabe daga Libya

Kotu ta fara binciken tsohon minista a gwamnatin Nicolas Sarkozy na Faransa, bisa zargin hannu wajen karbo kudaden yakin neman zaben tsohon shugaban kasar a 2007 daga Libya.

Eric Woerth na zantawa da RFI 5 ga watan  satumbar 2017.
Eric Woerth na zantawa da RFI 5 ga watan satumbar 2017. RFI
Talla

Tsohon minista Eric Woerth shi ne babban ma’ajin kudi na kwamitin yakin neman zaben Sarkozy, kuma har yanzu shi ne shugaban Kwamitin Kudade a majalisar dokokin Faransa.

A watan satumbar 2017 ne sashen binciken zargin  rashawa na rundunar ‘yan sandan kasar ya fara binciken tsohon ministan, dangane da rawar da ya taka wajen karbo makudden kudade daga tsohon shugaban Libya Mu’ammar Kadhaffi don tallafa wa yakin neman zaben Nicolas Sarkoz a 2007.

Sarkozy da kansa sau da dama yana gurfana a gaban ‘yan sanda da ke binciken zargin, kafin daga bisani a mika shi a hannun alkalai domin tuhuma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.