Arrangama tsakanin bakin haure da jami’an tsaro a Calais
A Faransa akalla bakin-haure biyar suka jikkata a birnin Calais na kasar, sakamakon arrangamar da aka yi tsakanin bakin hauren kasashen Afghanistan da kuma Eritria.
Wallafawa ranar:
Kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya ruwaito cewa yanzu haka, an garzaya da wasu bakin haure 4 ‘yan kasar Eritria asibiti, domin cire musu harsasan da aka harbe su da su.
Fadan wanda bakin hauren suka shafe kimanin sa’o’i 2 suna gwabzawa, ya fara ne a lokacin da bakin hauren ke bin layin karbar abinci.
Kimanin bakin-haure ‘yan kasar Eritria 100 da kuma na Afghanistan 30 rikicin ya rutsa da su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu