Isa ga babban shafi
Faransa

"Faransa ba za ta amince a kafa sansanin bakin haure ba"

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce, gwamnatinsa ba za ta amince da sake kafa wani sansanin bakin haure ba makamancin na dajin Calais a yankin arewacin kasar.

Shugaban Faranse Emmanuel Macron a yayin ziyararsa a yankin Calais
Shugaban Faranse Emmanuel Macron a yayin ziyararsa a yankin Calais Reuters
Talla

Macron ya bayyana haka ne a yayin gabatar da jawabi a ziyarar da ya kai yankin a dai dai lokacin da gwamnatinsa ke matsin lamba kan Birtaniya don ganin ta kara kaimi wajen bada gudun mawar daukan dawainiyar bakin hauren da ke kokarin shiga Birtaniya ta barauniyar hanya.

A cewar Macron, sun yi duk abin da ya kamata don hana bakin tsallakawa Birtaniya ba bisa ka’ida ba, kuma ya ce, ba za a yi amfani da dajin Calais ba a matsayin hanyar shiga Birtaniya ta bayan fage.

Tsohuwar gwamnatin Francois Hollande ce ta rusa sansanin na Calais mai cike da kazanta wanda ya kasance matsuguni ga bakin haure dubu 10

Sai dai har yanzu akwai tsirarun mutane da ke fakewa a sansanin da nufin samun sararin tsallakawa zuwa Birtaniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.