Isa ga babban shafi
EU

EU ta shigar da karar mambobinta a kotu saboda baki

Kungiyar Tarayyar Turai ta shigar da karar kasashen Jamhuriyar Czech da Hungary da Poland a gaban babbar kotun nahiyar saboda yadda suka ki karbar wani kaso na ‘yan gudun hijira da ke neman mafaka.

Kasashen Poland da Hungary da Jamhuriyar Czech sun ki karbar wani kaso na 'yan gudun hijira
Kasashen Poland da Hungary da Jamhuriyar Czech sun ki karbar wani kaso na 'yan gudun hijira REUTERS/Marko Djurica
Talla

Wannan matakin ya nuna jajircewar Kungiyar Tarayyar Turai wajen ganin cewa, mambobinta sun mutunta tsarin da aka samar a shekarar 2015 na karkasa ‘yan gudun hijira dubu 160 tsakanin kasashen Turai don rage nauyin da ke kan Girka da Italiya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a birnin Brussels, Hukumar Tarayyar Turai ta ce, ta yanke shawarar maka Jamhuriyar Czech da Poland da kuma Hungary a kotun shari’a saboda yadda suka yi watsi da hakkokin da suka rataya a wuyansu.

Kawo yanzu dai babu wani martani daga bangaren wadannan kasashe da a can baya suka ce, tilasta mu su karbar wani kaso na ‘yan gudun hijirar, wani yunkurin tauye mu su ‘yanci tafiyar da kasashensu ne.

A cikin watan jiya ne , Kungiyar Tarayyar Turai ta gargadi daukan mataki kan kasashen bayan tsawon lokacin da aka shafe tana gargadin su.

Yanzu haka dai kasashen na fuskantar barazanar biyan tara mai yawa a kotun da ke Luxembourg.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.