Isa ga babban shafi
Faransa-Daular Larabawa

''Ana gaf da murkushe IS'' a cewar shugaba Emmanuel Macron

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce nan ba da jimawa ba za a murkushe kungiyar IS musamman a kasashen Iraki da kuma Syria, to sai dai wannan ba ya nufin cewa an kawo karshen ayyukan ta’addanci a cewarsa.

Emmanuel Macron lokacin da ya ziyarci rundunar sojin Faransa a Abou Dhabi, ranar 9 ga watan nuwamba 2017.
Emmanuel Macron lokacin da ya ziyarci rundunar sojin Faransa a Abou Dhabi, ranar 9 ga watan nuwamba 2017. REUTERS/Ludovic Marin/Pool
Talla

Shugaba Macron wanda ke gabatar da jawabi ga sojojin Faransa da ke wani bariki a Abu Dhabi, ya ce sun yi nasara a kan mayakan na IS a garin Raqa, abin da ke tabbatar da cewa a cikin ‘yan watanni kadan masu zuwa za a murkushe kungiyar baki daya ta fannin soji.

To sai dai shugaban na Faransa ya bayyana cewa bayan murkushe kungiyar ta hanyar amfani da soji, mataki na gaba shi ne tabbatar da cikakken tsaro, abin da ya ce yana daukar dogon lokaci.

Barikin sojin Abu Dhabi, shi ne daya tilo da Faransa ta mallaka a wata kasa baya ga nahiyar Afirka, kuma an bude shi ne bayan kammala yakin tekun Pasha (1990-1991).

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.