Isa ga babban shafi
Tarayyar Turai

Tarayyar Turai ta kaddamar da sabon shirin karbar 'yan ci rani

Tarayyar Turai ta kaddamar da wani sabon shirin karbar baki ‘yan gudun hijira daga gabas tsakiya da kuma ‘yan ci ranin Afrika a wani mataki na haramta ratso tekun Bahrum mai hatsarin gaske inda kullum ake samun hasarar rayukan jama’a.

Karkashin sabon shirin Tarayyar Turai za ta gindaya karbar 'yan ci rani da 'yan gudun hijira kimanin dubu hamsin cikin shekara biyu.
Karkashin sabon shirin Tarayyar Turai za ta gindaya karbar 'yan ci rani da 'yan gudun hijira kimanin dubu hamsin cikin shekara biyu. Reuters
Talla

Shirin ya kunshi karbar ‘yan gudun hijira da ‘yan ci ranin Afrika nan da shekaru biyu a tsakanin mambobin Tarayyar Turai.

Babban jami’in kula da gudun hijira na Tarayyar Turai Dimitiris Abramopolous ya shaidawa taron manema labarai a Brussels cewa sun dauki matakin ne domin kawon karsshen hatsarin ratso tekun bahrum.

Hukumar Tarayyar Turai ta ce za ta bullo da tsarin karbar ‘yan ci ranin akalla dubu hamsim a shekaru biyu amma wadanda ke matukar bukatar taimakon kasashen duniya.

Akwai ‘yan gudun hijira dubu 23 da Tarayyar Turai ta karba da aka rarraba a sansanoni a mambobin kungiyar yawancinsu yan gudun hijirar rikicin Syria

Yanzu kuma Tarayyar Turai za ta mayar da hankali ga baki da ke kwarara daga Afrika yawanci daga Libya da Nijar da Masar da Chad da habasha da Sudan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.