Tarayyar Turai ta kaddamar da sabon shirin karbar 'yan ci rani
Tarayyar Turai ta kaddamar da wani sabon shirin karbar baki ‘yan gudun hijira daga gabas tsakiya da kuma ‘yan ci ranin Afrika a wani mataki na haramta ratso tekun Bahrum mai hatsarin gaske inda kullum ake samun hasarar rayukan jama’a.
Wallafawa ranar:
Shirin ya kunshi karbar ‘yan gudun hijira da ‘yan ci ranin Afrika nan da shekaru biyu a tsakanin mambobin Tarayyar Turai.
Babban jami’in kula da gudun hijira na Tarayyar Turai Dimitiris Abramopolous ya shaidawa taron manema labarai a Brussels cewa sun dauki matakin ne domin kawon karsshen hatsarin ratso tekun bahrum.
Hukumar Tarayyar Turai ta ce za ta bullo da tsarin karbar ‘yan ci ranin akalla dubu hamsim a shekaru biyu amma wadanda ke matukar bukatar taimakon kasashen duniya.
Akwai ‘yan gudun hijira dubu 23 da Tarayyar Turai ta karba da aka rarraba a sansanoni a mambobin kungiyar yawancinsu yan gudun hijirar rikicin Syria
Yanzu kuma Tarayyar Turai za ta mayar da hankali ga baki da ke kwarara daga Afrika yawanci daga Libya da Nijar da Masar da Chad da habasha da Sudan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu