Emmanuel Macron ya shiga rana ta biyu a ziyar da ya kai Girka
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bukaci asusun bayar da lamuni na duniya, IMF da ya nuna kyakkyawar aniya dangane da kokarin ceto Girka daga matsalar bashin da kasar ke fama da ita.
Wallafawa ranar:
Shugaba Macron ya fadi hake a birnin Athens a yayin da da ya ke gudanar da ziyarar kwanaki biyu a Girka, kuma a dai dai lokacin da ya rage watanni 11, wa’adin ceto Girka ya cika.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana cewa, muddin asusun na son taka rawa a shirin ceto Girka daga kangin bashi, to ya dace ya nuna kyakkyawar aniya ba tare da kara gindaya wa kasar wasu sharudda ba.
Karo na uku kenan da ake samar da tsare-tsaren fitar da Girka daga matsalar bashin, kuma a halin yanzu, kungiyar Turai ce ke daukar dawaniyar ceto kasar nan da watan Agustan 2018.
IMF ya ce, ba zai sanya kobo ba a shirin ceto Girka daga bashin har sai wadanda ke bai wa kungiyar tarayyar Turai rance sun dada sassauta wa Girkan dimbin bashin, abin da har yanzu ake kai ruwa rana musamman ganin yadda Jamus ke ci gaba da nuna tirjiya.
Shugaba Macron ya nuna damuwa da matakin da kungiyar ta EU ta dauka na neman agaji daga waje kafin samun nasarar ceto Girka a shekarar 2010, abin da ya fito da rashin jituwa tsakanin kasashen yankin da wasu manyan cibiyoyi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu