An fara tattaunawar ficewar Birtaniya daga Tarayyar Turai
An fara tattaunawar karshe tsakanin wakilan Birtaniya da na kungiyar Tarayyar Turai, domin shata yadda Birtaniya za ta kammala ficewa daga kungiyar kamar yadda ‘yan kasar suka butaka ta hanyar kuri’ar raba gardama da suka kada a bara.
Wallafawa ranar:
Tattaunawar na zuwa, kwanaki kadan bayan da Firaminista Theresa May ta rasa rinjaye da take da shi a majalisar dokokin kasar, lamarin da ake ganin zai iya haifar wa Birtaniya tarnaki a tattaunawar.
Jagoran tattaunawar a bangaren Tarayyar Turai Michel Bernier ya tabbatar da soma tattaunawar bayan ya gana da ministan Birtaniya David Davis a Brussels a yau Litinin.
Akwai muhimman batutuwa guda uku da Birtaniya ke son tattaunawar ta fi mayar da hankali akai kafin tattauna makomar kawancenta da Tarayyar Turai.
Birtaniya na son Tarayyar Turai ta biya ta kudin ficewa da suka kai biliyan 100 na yuro.
Akwai kuma batun makomar ‘yan kasashen Tarayyar Turai sama da miliyan uku a Birtaniya da ‘Yan Birtaniya a sassan Tarayyar Turai da batun makomar rikicin kan iyaka tsakanin Jamhuriyyar Ireland da arewacin Ireland.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu