Isa ga babban shafi
Faransa

Zaben Faransa: Macron da Le Pen za su fafata a zagaye na biyu

Sakamako daga rumfunan zaben kasar Faransa ya nuna cewa, dan takar mai zaman kansa Emmanuel Macron ne ke kan gaba a kuri’un da aka kada a zagayen farko na zaben shugabancin kasar da aka gudanar.

Emmanuel Macron ke kan gaba a zagaye na farko da kuri'u kashi 23 Marine Le Pen ce ta biyu da kashi 21
Emmanuel Macron ke kan gaba a zagaye na farko da kuri'u kashi 23 Marine Le Pen ce ta biyu da kashi 21
Talla

Mai ra’ayin kishin kasar ta jam’iyyar National Front Marine Le Pen ke biye da Macron a matsayi na biyu, wanda hakan ya ba su damar zuwa zagaye na biyu  za a yi a ranar ga 7 ga watan Mayu mai zuwa.

Macron na da kashi 23 zuwa 24 na kuri’un da aka kada yayin da Le Pen ke da kashi 21 zuwa 23.

Masu hasashe dai na ganin cewa Emanuel Macron mai shekaru 39 zai iya lashe zaben shugabancin Faransa, wanda sakamakonsa ke da tasiri kan Kungiyar Tarayyar Turai EU.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.