Isa ga babban shafi
Faransa

Hukumomin Faransa na bincike kan maharin Paris

Masu shigar da kara a Faransa na binciken asalin maharin da ya kashe jami’in ‘yan sanda guda a wani hari da ya kaddamar a kasaitacciyar unguwar Champs Elysees da ke birnin Paris. 

Masharhanta sun ce harin Paris zai iya yin tasiri dangane da fitowar jama'a don kada kuri'unsu a zaben Faransa
Masharhanta sun ce harin Paris zai iya yin tasiri dangane da fitowar jama'a don kada kuri'unsu a zaben Faransa REUTERS/Christian Hartmann
Talla

Wannan na zuwa ne a yayin da ake shirin gudanar da zagayen farko na zaben shugabancin kasar a gobe Lahadi.

Harin wanda kungiyar ISIS ta ce ta na da hannu a cikinsa, ya janyo musayar ra’ayoyi tsakanin ‘yan takarar kan yadda za a samar da tsaro a Faransa.

Masu sharhi sun bayyana cewa, harin na ranar Alhamis da ta gabata, zai iya yin tasiri dangane da fitowar jama’a don kada kuri’unsu a zaben.

Tuni dai jami’an tsaro suka kashe maharin mai suna Karim Cheurfi kuma dan shekaru 39.

Hukumomin tsaron Faransa za su jibge jami'an 'yan sanda dubu 50 da kuma sojoji dubu 7 don bai wa masu kada kuri'u a zaben na gobe kariya a duk fadin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.