Isa ga babban shafi
Birtaniya

Bamu yi wa kungiyar tarayyar turai barazana ba - Johnson

Sakataren harkokin wajen Birtaniya Boris Jonhson, ya musanta cewa gwamnatin kasar ta yi barazanar rage tallafinta kan yaki da ta’addanci a nahiyar turai muddin ba’a samar da sabuwar yarjejeniyar kasuwanci tsakaninta da kungiyar EU kafin ficewarta daga karkashinta ba.

Sakataren harkokin waje na Birtaniya Boris Jonhson a taron ministocin harkokin waje na kasashen da ke karkashin kungiyar tsaro ta NATO a birnin Brussels, kasar Belgium a ranar 31 ga watan Maris shekara ta 2017.
Sakataren harkokin waje na Birtaniya Boris Jonhson a taron ministocin harkokin waje na kasashen da ke karkashin kungiyar tsaro ta NATO a birnin Brussels, kasar Belgium a ranar 31 ga watan Maris shekara ta 2017. REUTERS/Virginia Mayo/Pool
Talla

Yayin zantawarsa da jaridar Le Figaro da ake wallafawa a Faransa, Johnson ya ce bada gudunmawa wajen tabbatar da tsaro a nahiyar turai abu ne muhimmi ga Birtaniya.

Johnson ya ce Birtaniya zata cigaba da aiki tare da kungiyar tarayyar turai EU, domin kare nahiyar daga barazanar ta’addanci bayan ficewar kasar daga karkashin kungiyar.

An dai rawaito cewa, cikin wasikar da ta aikewa kungiyar tarayyar turai, Firaministan kasar Birtaniya Theresa May, ta ce mai yiwuwa ne gudunmawar kasar kan yaki da ta’addanci ya ragu, muddin ta fice daga karkashin kungiyar, ba tare da cimma sabuwar yarjejeniyar cinikayya da ita ba.

Sai dai fadar gwamnatin Birtaniya ta ce kalaman Firaministan ba barazana ba ce don tilasta biya mata bukata. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.