Mutane 37 sun mutu a hadarin jirgin Turkiya
Akalla mutane 37 suka mutu da suka hada da yara kanana bayan faduwar wani jirgin sama mai dakon kaya na Turkiya kusa da filin saukar jirgin Bishkek babban birnin kasar Kyrgyzstan.
Wallafawa ranar:
Talla
Hukumomin lafiya a Kyrgyzstan sun ce mutanen yankin da jirgin ya fadi ne suka fi mutuwa kuma cikinsu akwai yara kanana guda 6. Sannan matukan jirgin guda hudu ne suka mutu.
Faduwar jirgin kuma ya lallata gidaje akallla 43 a kauyen Datcha Souou da ya fadi. Rahotanni sun ce kuskure daga matukun jirgin ne ya yi sanadin faduwar jirgin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu