Isa ga babban shafi
Faransa

Majalisar Dinkin Duniya ta yaba da matakin kotun kolin Faransa

Majalisar Dinkin Duniya ta yaba da matakin da kotun kolin kasar Faransa ta dauka na watsi da dokar sanya kayan matar da ya haifar da zazzafar mahawar a kasar, inda take cewa matakin ya haifar da tsangwamar addini.  

Wata Musulma sanye da Burkin a gabar ruwan Faransa
Wata Musulma sanye da Burkin a gabar ruwan Faransa REUTERS/Baz Ratner
Talla

Mai Magana da yauwn hukumar kare hakkin Bil Adama ta Majalisar Rupert Colville, yace irin wannan mataki da wasu garuruwan Faransa suka dauka baya samar da tsaro sai dai haifar da tsangwamar addini musamman ga mata Musulmai da ke kasar.

Majalisar tace irin wannan doka na shafar mata wajen tauye musu hakkokin su da kuma hana su zabin irin kayan da suke so su saka.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.