Isa ga babban shafi
Faransa

'Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane a cocin Faransa

Wani limamin cocin Faransa ya rasa ransa bayan wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da jama’a a cikin cocin wanda ke kusa da birnin Rouen na arewacin kasar.

Jami'an tsaron Faransa sun killace wurin da garkuwar ta faru
Jami'an tsaron Faransa sun killace wurin da garkuwar ta faru CHARLY TRIBALLEAU / AFP
Talla

‘Yan bindigar sun kutsa cikin cocin ne a lokacin da ake gudanar da bauta, inda suka yi garkuwa da limamin da wasu daga cikin masu ibada.

Kafofin yada labaran Faransa sun rawaito cewa, an jin karar harbe -harben bindiga bayan jami’an tsaro sun isa wurin, inda suka kashe ‘yan bindigar guda biyu.

Tuni dai aka killace wurin da lamarin ya faru yayin da hukumomi suka bukaci jama’a da su kauracewa wurin.

Shugaban Faransa Francois Hollande da ministan cikin gida Bernard Cazeneuve na kan hanyarsu ta zuwa birnin na Rouen don sanin halin da ake ciki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.