Isa ga babban shafi
Jamus

Hadarin jirgi: Gwamnatin Jamus ta kaddamar da bincike

Gwamnatin Jamus ta kaddamar da bincike kan yadda jiragen fasinjan kasar guda biyu da ke amfani da birki na musamman suka yi taho mu gama, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 10, yayin da wasu da dama suka samu rauni.

Hadarin jirgin ya yi sanadiyar mutuwar mutane 10
Hadarin jirgin ya yi sanadiyar mutuwar mutane 10 AFP
Talla

'Yan sandan kasar sun tabbatar da mutuwar mutanen 10, tare da fadin cewa mutane 18 sun samu rauni matuka, yayin da wasu 63 suka samu rauni masu sassauci.

Shugabar gwamnatin kasar Angela merkel ta bayyana kaduwarta da hadarin jiragen na kasa.

A shekara ta 2011 ne Jamus ta dauki wasu matakan kariya ta hanyar dasa wasu na’urori da aka fi sani da PZB 90 da ke iya daidaita birkin jirgin kasa muddun ya yi kuskuren sakin hanya, sai dai ga dukkan alamu tsarin bai yi tasiri ba ganin munin hadarin na jiya da ya jefa kasar cikin jimami.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.