An janye dakarun tsaro daga wani masallaci dake Brussels
Ma’aikantan agaji sun kai samame babban Masallaci dake Brussels a kasar Belgium inda suka kwashe masallatan dake ciki, suka kuma baiwa wasu mutane 11 magani bayan an gano wani kumshi wanda daga baya aka gano cewar garin filawa ne.
Wallafawa ranar:
Kakakin ma’aikatar agajin kasar, Pierre Meys yace sun cire kawanyar da suka yiwa Masallacin bayan sun tabbatar da cewar mutanen dake cikin sa basa fuskantar wata barazana.
Kasar Belgium na daya daga cikin kasashen da ake daukar matakan tsaro dan kaucewa harin ta’addanci bayan harin da aka kai Paris ranar 13 ga watan Novemba wanda ya hallaka mutane 129.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu