Isa ga babban shafi
Faransa

Birtaniya ta goyi bayan Faransa akan fada da IS

Shugaban Faransa Francois Hollande ya samu goyon bayan Firaministan Birtaniya David Cameron kan yakin da ya kaddamar da mayakan IS masu da’awar jihadi a duniya.

Shugaban Faransa Francois Hollande tare da David Cameron na Birtaniya a fadar  Elysee a birnin Paris
Shugaban Faransa Francois Hollande tare da David Cameron na Birtaniya a fadar Elysee a birnin Paris REUTERS/Eric Gaillard
Talla

Shugabannin sun gana ne a ranar Litinin kan jerin munanan hare haren da aka kai ranar Juma’a 13 ga watan Nuwamba a Paris.

Firamnistan Birtaniya David Cameron ya kai ziyara a Bataclan gidan cashewar da ‘Yan bindiga suka kashe mutane 90 tare da garkuwa da wasu a Paris.

Cameron ya bayyana goyon bayansa ga Hollande na kai wa mayakan IS hare hare ta sama a Syria.

Sannan Firamnistan ya bayyana cewa Birtaniya ma zata shiga cikin sahun kasashen da ke kai hari ta sama akan IS, kamar yadda Hollande ya tabbatar bayan ganawarsa David Cameron a Paris.

Cameron ya kuma ba Faransa damar yin amfani da sansanin jiragen sojinta a Cyprus domin shirya kai wa IS hari.

Nan gaba Hollande zai gana shugabannin kasashen Amurka da Rasha da Jamus kan yaki da mayakan IS.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.