Wasu Musulmin Bosnia na son a hukunta Kwamandojin MDD
Iyalan wasu Musulmin Bosnia uku da aka kashe lokacin da suke barin sansanin Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 1995 sun bukaci kotun kare hakkin Bil Adama ta kasashen Turai da ta gurfanar da kwamandojin Majalisar guda 3 saboda sakacin da suka yi aka kashe su.
Wallafawa ranar:
Matakin ya biyo bayan hukuncin wata kotun Holland da ta ki yarda a gurfanar da kwamnadojin guda uku.
Sojojin Serbia a karkashin jagorancin Ratko Mladic ne suka kashe Musulmin maza da yara kusan 8000, a shekarar 1995, kisan kiyashi mafi muni da aka bayyana tun kawo karshen yakin duniya na biyu.
Kwamandojin kasar Holland ne Musulmin na Bosnia ke son a hukunta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu