Isa ga babban shafi
Switzerland

Hollande zai gabatar da jawabi ga taron Davos

Yau juma’a ana ci gaba da gudanar da taron tattalin arzikin duniya a birnin Davos na kasar Suisse, taron da ke samun halartar masana tattalin arziki da kuma masu fada-a-ji a siyasar duniya.

Taron tattalin arzikin duniya a Davos
Taron tattalin arzikin duniya a Davos REUTERS/Ruben Sprich
Talla

A wannan juma’a shugaba Francois Hollande na Faransa zai gabatar da jawabi a gaban mahalarta taron sama da dubu biyu, kuma batun tattalin arziki musamman matsalolin kudi da Faransa da sauran kasashen Turai ke fama da su za su mamaye jawabin nasa.

Wasu daga cikin muhimman batutuwan da taron na Davos ke tattaunawa sun hada da sha’anin tsaro da kuma barazanar ta’addanci, yayin da faduwar farashin man fetur a duniya ke matsayin muhimmi ga mahalarta taron na bana.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.