Firaministan Bulgaria ya yi murabus tare da gwamnatinsa
Firaminsitan kasar Bulgaria ya yi murabus tare da gwamnatinsa domin amsa kiran ‘yan kasar da suka kwashe kwanaki suna zanga-zzanga. Wannan ne kuma ya bude kofar gudanar da sabon zabe a kasar. Firaminsitan kasar Boyko Borisov, ya ce ya yi murabus ne domin ba ‘Yan kasar ‘yancinsu da suka zabe su.
Wallafawa ranar:
“Bazan saka kaina a cikin gwamnatin da ‘yan sanda ke muzgunawa jama’a ba, ko kuma inda aka maye gurbin tattaunawa da barazana.” Inji Borisov.
A watan Aprilu mai zuwa ne ake sa ran za a gudanar da zabe, inda a yanzu haka Shugaban kasar zai zabi gwamnatin rikon kwarya domin tafiyar da harkokin kasar kamin zaben.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu