Isa ga babban shafi
Norway

Kotun Norway ta daure Mutane biyu da Laifin Ta'addanci

Wata kotu a Oslo na kasar Norway ta daure wasu mutane biyu yau, saboda shirin kai mummunar hari bama-bamai kan kamfanin buga jaridar Denmark mai suna Jyllands-Posten, wadda ta yi wasu munanan kalamai da zane da suka danganta da Manzo Annabi Muhammadu (SAW).

REUTERS/ABC Nyheter via Scanpix
Talla

Mutanen biyu Mikael Davud wanda aka daure na tsawon shekaru bakwai, sai kuma Shawan Sadel Saeed Bujak wanda aka daure na tsawon shekaru uku da rabi

Kotun ta ce ta gamsu cewa jaridar wadda ta buga munanan bayanan, a watan bakwai na 2010, mutanen biyu sun tsara babbaka ofishin jaridar sannan kuma su kashe marubucin kalaman sabon.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.