A makon daya gabata gwamnonin Najeriya, karkashin jam’iyyar APC mai mulkin kasar, suka bayar da sanarwar daukar matakan yaki da talauci, ta hanyar samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar.
Gwamnonin sun bayyana hakan ne a lokacin da suka kammala taronsu a Yolan Jihar Adamawa, inda kuma suka kafa wani kwamitin da zai samar da hanyoyin yaki da talaucin.
Dama dai jihar Jigawa, dake arewacin kasar ta fara wani shirin hadin gwiwa da rukunin kamfanonin Dangote, don farfado da tattalin arzikin jihar, ta hanyar samar da katafariyar ma’aikatar shinkafa a Jihar.
wannan ne abinda Nasiruddeen Muhammad ya duba cikin shirin Kasuwa a kai miki Dole, ayi saurare lafiya...
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu