Guatemala
Mutane 30 sun mutu, wasu 600 sun bata, sakamakon a zaftarewar kasa a Guatemala.
A kalla mutane 30 ne suka rasa rayukansu a kasar Guatemala a yayinda wasu sama da 600 suka bata sakamakon zaftarewar kasa da ta rutsa da daruruwan gidajen zaman jama’a dake kusada babban birnin kasar
Wallafawa ranar:
Talla
Yanzu haka dai sama da masu aikin ceto 500 ne, ke ci gaba da kokarin tono wadanda hadarin ya rutsa da gidajensu, bayan da aka dakatar da aikin ceton a daren jiya juma'a
Hadarin dai ya faru ne, tsakanin daren shekaranjiya Alhamis zuwa safiyar jiya juma’a, a wani wuri mai tazarar kilo mita 15 gabashin Santa Catarina Pinula babban birnin kasar ta Guatemala
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu