Kasar Masar ta rabu gida biyu bayan da Sojoji suka tumbuke gwamnatin 'Yan uwa Musulmi ta Shugaba Morsi. 'Yan uwa Musulmi sun sha alwashin kalubalantar matakin, a dai dai lokacin da 'Yan adawa a karkashin Mohammed El Baradei ke murnar samun nasara. Wannan shi ne batun da shirin Duniyarmu A yau ya tattauna wanda Bashir Ibrahim Idris ya jagoranta.