Ilimi Hasken Rayuwa
Wannan Shirin ya shafi Fadakar da al'umma game da ci gaban da aka samu a sha'anin Ilimi a fannoni daban-daban na duniya, tare da nazari kan irin ci gaban da aka samu wajen binciken kimiya da fasaha da ke neman saukakawa Dan’adam wajen tafiyar da rayuwarsa a duniya. Shirin kuma zai yi kokarin jin irin bincike da masana ke yi domin inganta rayuwar Bil’adama. Shirin na zo maku ne, a duk ranar Talata a shirye-shiryenmu na safe, a ku maimata ranar Alhamis.
Ci gaban karatuSaurari kashin karshe
-
Karuwar masu mallakar takardun kammala karatu na bogi a Najeriya, na barazana ga karewar kwararru
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan mako ya duba yadda mallakar takardun kammala karatu na bogi a Najeriya ke barzana ga karewar kwararru a fannoni da dama.26/03/202410:00 -
An samar da cibiyar sadarwa a jahar Bauchi don saukakawa dalibai wajen bincike
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa a wannan lokacin ya yi duba ne kan yadda wasu kungiyoyi karkashin cibiyar fasahar sadarwa da ci gaban al’umma wato CITAD suka samar da wata katafariyar cibiyar sadarwa da aka yiwa lakabi da HELLO HOPE a jahar Bauchi. Shirin ya kasance wani bangare na yunkurin saukakawa mazauna karkara hanyoyin samun sadarwa ta internet musamman wuraren da babu irin wannan ci gaba ko kuma wuraren da suke da shi amma bashi da karfi, wanda jama’are ke cikin wannan rukuni.19/03/202409:47 -
Taro kan gudummawar kafafen yada labarai a bangaren tsaro a jami'ar ABU Zaria
Matsalar tsaro na daya daga cikin matsalolin da ke addabar Najeriya, musamman ma arewacin kasar, hakan ya sanya sashen koyon aikin jarida na jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria da ke jihar Kaduna ya shirya wani taro gagarumin taro na kasa da kasa domin tattaunawa a kan gudumawar da kafafen yada labarai za su iya bayarwa wajen warware matsalar tsaro. Ya yi wannan ne da zummar taimaka wa kokarin da al'umma ke yi wajen warware wa kansu matsalar tsaron da ke damun su.05/03/202409:57 -
Yadda dalibai ke barin karatu a Nijar don tafiya neman kudi a wasu kasashe
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa a wannan lokacin ya yi duba ne kan yadda dalibai da dama a Jamhuriyar Nijar, musaman maza ke barin karatu da sunan tafiya neman kudi, kasashen ketare kamar Libiya, Aljeriya ko kuma hako zinare a kasar Mali kai harma da kokarin tsallakawa Turai, abin da ya sanya kungiyoyin dalibai a kasar bazama aikin wayar da kan matasa kan sanin muhimmancin da ilimi ke da shi.27/02/202410:09 -
Yadda gwamnatin jahar Neja ta fara horas da dalibai sana'oin dogaro da kai
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon zai yi duba ne kan yadda gwamnatin jahar Neja da ke Arewacin Najeriya, ta samar da shirin horas da dalibai sana'oin hannu don dogaro da kai. Gwamnatin jahar dai ta ware ranar Juma'ar kowane mako don gudanar da darasin koyon sana'oin hannu.20/02/202410:05 -
Yadda amfani da komfuta ya shafi kyaun rubutun dalibai
A wannan makon zamu duba yadda ci gaban kimiyya da Ilimi ke zama wani nau’I na koma baya musamman a tsakanin dalibai a Najeriya.Tun bayan samar ko kuma kirkirar na’urar kwamfuta a 1837, da kuma shigowar ta Najeriya karon farko a 1963 sannu a hankali take bazuwa tsakanin jama’a, yayi da kuma ake samun ci gaba ta fannin amfani da ita.31/01/202409:34 -
Gwamnatin Neja na shirin farfado da tsarin karatun makiyaya
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon zai yi duba ne da tsarin karatun 'yayan makiyaya, wato Nomadic Education. Gwamnatin jihar Neja ce ta yi hobbasa don farfado da shirin karatun 'yayan makiyaya a jihar. Shirin zai bai wa makiyaya damar samun ilimi a duk inda suka yi balaguro don inganta makomarsu. Yanzu haka dai shirye-shirye sun yyi nisa a game dfdaa wannan shirin a jihar Neja mai fara da matsalar tsaro sakamakon ayyukan 'yan bindiga da ke kashe mutane da satar su don kudin fansa.19/12/202309:56 -
Taimakon da kirkirarren Tabarau ke bai wa masu fama da matsalar raunin gani
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon tare da Shamsiyya Haruna ya maida hankali ne kan nazarin da masana kimiya suka yi wajen kirkirar Tabaraun hangen nesa, don taimakawa masu raunin gani. A jamhuriyar Nijar, matsalar gani na zama babban kalubale ga al'ummar kasar wacce a yanzu har aka fara samunta a tsakanin matasa.28/11/202310:04 -
Iyayen dalibai a Nijar na kokawa kan tsadar kudin karatu
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon tare da Shamsiyya Haruna ya maida hankali ne kan yadda iyaye ke kokawa a jamhuriyar Nijar kan tsadar kudin karatun 'ya'yansu, masamman makaruntu masu zaman kansu saboda matsaloli na tsadar rayuwa da aka shiga tun bayan da sojoji suka yi juyin mulki.14/11/202310:08 -
Najeriya: Yadda tsadar man fetur ke ci gaba da yin tasiri kan harkar ilimi
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan mako tare da Shamsiyya Haruna ya maida hankali ne kan yadda matsalar tsadar man fetur ke ci gaba da yin tasiri akan harkar ilimi a Najeriya, wanda tun bayan sanar da janye tallafin mai a kasar kanana da manyan makarantu ke daukan matakai daban daban da zummar daidaita harkokinsu a cikin wannan yanayi.31/10/202310:06 -
Yadda za'a karfafa ilimin fasaha a Najeriya
Shirin ilimi hasken rayuwa na wannan mako ya duba taron fayyace zakakuran matasan da ke da fasahar zamani don karfafa musu gwiwa da fadada ilimin su.24/10/202310:11 -
Tsarin koyar da ilimin Computer ga daliban da ke shirin shiga jami'a a Nijar
Shirin Ilimi hasken rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali kan tasirin ilimin fasahar na'ura mai kwakwalwa ko kuma computer ga daliban da ke shirin shiga jami'a a Jamhuriyyar Nijar, sabon tsarin da aka bijiro da shi da nufin taimakawa tarin daliban da basu da gogewa a fannin na fasahar na'urar computer.10/10/202310:17 -
Gudunmowar ilimin sararin samaniya ga ci gaban duniya
Shirin Ilimi hasken rayuwa na wannan mako ya yi duba ne kan irin rawar da nazarin ilimin sararin samaniya ke bada gudunmowa wajen habbaka ci gaban duniya.12/09/202310:04 -
Yadda dalibai ke gaza cin jarabawa ta komfuta
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan mako ya yi duba ne da yada dalibai ke faduwa a jarabawar da ake yi da na'urar komfuta, wato CBT exams. Dallibai dai na yawan kokawa a kaan yadda sukaa faduwa sosai a irin wannan jarabawa, sabanin wadda suka saba, ta alkalami da takarda. Hasali ma daliban naa gaanin cewa matsalar ba daga gare su take ba, inda suka kawo dalilai da dama da ke nnuna cewa ba su daa laifi don sun fadi irin wannan jarabawar.15/08/202310:14 -
Taron kungiyar malaman jaami'o'in shiyyar arewa maso yammacin Najeriya
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan makon ya mayar da hankali ne kan taron kungiyar malaman jami'o'in shiyyar arewa maso yammacin Najeriya. Makasudin wannan taro kamar yadda kungiyar ta bayyana shine nazari kan irin ci gaban da aka samu ko akasinsa a jam'i'o'in shiyyar da zummar lalubo hanyoyin samun mafita.01/08/202310:14
Wannan Shirin ya shafi Fadakar da al'umma game da ci gaban da aka samu a sha'anin Ilimi a fannoni daban-daban na duniya, tare da nazari kan irin ci gaban da aka samu wajen binciken kimiya da fasaha da ke neman saukakawa Dan’adam wajen tafiyar da rayuwarsa a duniya. Shirin kuma zai yi kokarin jin irin bincike da masana ke yi domin inganta rayuwar Bil’adama. Shirin na zo maku ne, a duk ranar Talata a shirye-shiryenmu na safe, a ku maimata ranar Alhamis.