Bakonmu a Yau
Mataimakin magajin garin Abala Boubacar Oumarou kan tashe-tashen hankula akan iyakar Nijar da Mali
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:25
Shugabannin al’ummomin da ke rayuwa a kan iyakar Mali da Jamhuriyar Nijar, sun dauki alkawarin shawo kan tashe-tashen hankulan da ke faruwa yankin.Shugabannin al’ummar, sun dauki wannan alkawarin ne a lokacin wani taron kwanaki uku da aka gudanar a garin Abala da ke jihar Tillabery da ke yammacin jamhuriyar Nijar.Mataimakin magajin garin Abala Honorable Boubacar Oumarou, ya yi mana karin bayani a game da wannan taro wanda shi ne irinsa na uku tsakanin al’ummomin da ke rayuwa a yankin.