Isa ga babban shafi
Nijar

Boko Haram ta kashe masu hakar man fetir a Nijar

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton mayakan Boko Haram ne, sun kashe ma’aikatan kamfanin Foraco 7 da ke aikin hakar rijiyoyin mai a garin Tumour da ke jihar Diffa ta Jamhuriyar Nijar.

Garin Diffa na fama da hare-haren Boko Haram
Garin Diffa na fama da hare-haren Boko Haram AFP PHOTO / PIUS UTOMI EKPEI
Talla

Harin wanda aka kaddamar a safiyar ranar Alhamis ya auku ne a dai dai lokacin da jami’an tsaron da ke kare lafiyar ma’aikatan kamfanin suka janye daga fadar magajin garin Tumour, wato masaukin ma’aikantan kamfanin na Foraco.

Maharan sun yi awon gaba da motocin kamfanin guda biyu , yayin da suka kama hanyar zuwa kan iyakar Nijar da Najeriya.

Garin Tumour ya kasance wani sansanin ‘yan gudun hijira tun bayan da ‘yan Kungiyar Boko Haram suka fara kai hare-hare a kasashen da ke yankin tafkin Chadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.