Isa ga babban shafi
Niger

Mace ta farko da ta fara aikin jarida a Nijar ta rasu

Mace ta farko da ta fara aikin jarida a Jamhuriyar Nijar, Mariam Keita ta rasu tana da shekaru 72 a duniya, bayan tayi fama da rashin lafiya.

Mariam Keita, Mace ta farko da ta fara aikin jarida a Jamhuriyar Nijar.
Mariam Keita, Mace ta farko da ta fara aikin jarida a Jamhuriyar Nijar. YouTube
Talla

Wani na kusa da 'yar jaridar Ibrahim Moussa ne ya sanar da labarin rasuwarta, yayin da kafofin yada labaran kasar suka yada shi.

An dai haifi Mariama Keita a shekarar 1946 cikin Birnin Yammai, kuma itace Daraktar farko ta tashar Radiyo Sahel, mallakar gwamnati a matsayin Edita da kuma mai gabatar da labarai.

Tsakanin shekarar 2003 zuwa 2006 ta zama shugabar Majalisar Sadarwar gwamnati da dake sa ido kan harkar sadarwa a Nijar.

Keita na daga cikin Yan kungiyoyin fararen hula da kungiyar mata, wadda ta taka rawa wajen fadakar da jama’a kan fahimtar kundin tsarin mulki da y abada damar gudanar da zaben dimokiradiya na farko a shekarar 1993.

Mutuwar na ta na zuwa ne kwanaki bayan mutuwar Amadou Ousmane, tsohon Darakan Hukumar yada labarai kuma mawallafin kan matsalar cin hanci a kasashen Afirka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.