Isa ga babban shafi
Nijar

Kotu ta bada umarnin bude gidan rediyon Nijar

Wata Kotu a Jamhuriyar Nijar ta bada umurnin bude gidan rediyon Labari da gwamnati ta rufe a karshen mako saboda zargin cewar yana tinzira jama’a wajen tada hankali.

Gwamnatin Nijar na zargin gidan rediyon da tinzira jama'a wajen bore
Gwamnatin Nijar na zargin gidan rediyon da tinzira jama'a wajen bore Flickr/Curtis Kennington/CC/http://bit.ly/2mfKZKs
Talla

Alkalin kotun ya bayyana matakin rufe tashar a matsayin abin da ya saba ka’ida, in da ya bukaci jami’an tsaron da suke girke a tashar da su san in da dare ya yi musu.

Ali Idrissa, daya daga cikin shugabannin da suka shirya zanga zangar adawa da harajin gwamnati na can tsare a gidan yari tare da sauran abokan tafiyarsa.

Ministan cikin gida, Bazum Muhammed ya zargi tashar da zama bakin 'yan adawa wajen tinzira al’ummar kasar su yi mata bore.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.